Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin masu saurare kan rahoton NBS na ƙaruwar tattalin arziƙin Najeriya

Informações:

Synopsis

Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce tattalin arzikin ƙasar ya samu ƙarin tagomashi da kashi 3 da ɗigo 13 a rubu’in farko na wannan shekarar ta 2025, saɓanin kashi 2 da ɗigo 27 yake a daidai wannan lokaci a shekarar 2024.   Wannan na zuwa ne yayin da talauci ke ci gaba da ta’azzara a tsakanin al’ummar ƙasar, kuma manoma sun gaza yin noma yadda ya kamata saboda matsalar ta’addanci. Latsa alamar sauti domin sauraren shirin...