Wasanni
Yadda aka fafata a gasar kofin Sardauna ta tsoffin 'yan wasan arewacin Najeriya
- Author: Vários
- Narrator: Vários
- Publisher: Podcast
- Duration: 0:10:00
- More information
Informações:
Synopsis
Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar da tsofaffin ƴan wasan Najeriya da suka fito daga jihohin Arewacin ƙasar suka fafata. A makon daya gabata ne garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, ya karɓi baƙuncin gasar kofin Sardauna karo na 13, wacce tsofaffin ƴan wasan da suka fito daga jihohi 19 na Arewacin Najeriya suka ƙirƙira da zummar sada zumunci da kuma haɗa kan jihohin arewacin ƙasar. Tawagar da ta wakilci jihar Kebbi a wannan gasa ce dai ta yi nasarar lashe wannan kofi, bayan da ta doke takwararta ta Kano a bugun daga kai sai mai tsaron gida da ci 4-3. Latsa alamar sauti don sauraren shirin tare da Khamis Saleh...