Synopsis
A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.
Episodes
-
Najeriya: 'Yansanda sun karɓi umarnin kotu na dena kama masu baƙi gilashin mota
09/10/2025 Duration: 03minRundunar Ƴansandan Najeriya ta sanar da karɓar umarnin kotu na dakatar da kama motocin dake ɗauke da bakin gilashi, inda ta umarci jami'an ta da su dakatar da kamen har zuwa lokacin da za'a kammala shari'ar. Wannan ya biyo bayan rugawa kotu da wasu lauyoyi suka yi domin hana aiwatar da dokar da suka ce za ta take haƙƙin Bil Adama. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Barr Suleiman Muhammed, lauya mai zaman kansa. Ku latsa alamar sauti domin jin tattaunawarsu...
-
Malam Ibrahim Garba Wala game da wanda ya dace ya maye gurbin Yakubu a INEC
08/10/2025 Duration: 03minShugaban Hukumar zaɓen Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya kawo ƙarshen aikin sa a INEC, inda ya miƙa ragamar tafiyar da hukumar ga May Agbamuche.Yayin miƙa ragamar aikin, Yakubu ya roƙi kwamishinonin hukumar da su bai wa Agbamuche haɗin kai wajen gudanar da ayyukan ta na riƙo zuwa lokacin da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai naɗa wanda zai maye gurbinsa.Tuni dai tambayoyi suka yawaita game da wanda zai maye gurbin Yabubu a matsayin shugaban hukumar ta INEC, dangane da wannan batu Bashir Ibrahim Idris ya tattaunawa da Malam Ibrahim Garba Wala. Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar..........
-
Tattaunawa da Abdulhakeem Garba Funtua kan cika shekaru 2 da yaƙin Gaza
07/10/2025 Duration: 03minYau ake cika shekaru biyu cif da ƙazamin harin da Mayaƙan Hamas suka kai Isra'ila wanya ya hallaka Yahudawa fiye da dubu guda sanadiyyarsa ne kuma aka faro wannan yaƙi na Gaza da ya kashe Falasɗinawa fiye da dubu 60. Wannan yaƙi shi ne mafi muni da duniya ta gani a wannan ƙarnin wanda ya rushe fiye da kashi 90 na gine-ginen yankin. Dangane da wannan ne Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin siyasar ƙasashe don jin tasirin wannan yaƙi ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakkiyar hirar...
-
Tattaunawa da Alhaji Ouba Danlami game da babban zaɓen Kamaru
06/10/2025 Duration: 03minA Kamaru ana ci gaba da yaƙin neman zaɓen shugabancin ƙasar wanda za a gudanar ranar lahadi mai zuwa 12 ga wannan wata na Oktoba, inda ƴantakara 10 ke shirin fafatawa ciki har da shugaba mai-ci Paul Biya. Akwai dai waɗanda suka janye daga zaɓen don mara wa wasu ƴantakarar duk da cewa an tantance su, yayin da wasu suka yanke shawarar mara wa wasu ƴantakarar haka kawai saboda wasu dalilai. Alhaji Ouba Danlami, ya sha tsayawa takarar shugabancin ƙasar a zaɓukan da suka gabata, to amma ban da wannan karo, ko saboda? Ga ƙarin bayanin da ya yi wa Ahmed Abba. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar..