Bakonmu A Yau

  • Author: Vários
  • Narrator: Vários
  • Publisher: Podcast
  • Duration: 1:21:57
  • More information

Informações:

Synopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodes

  • Dr Yahuza Getso kan yadda jami'an sojoji suka hallaka Kachalla Ɗanbokolo a Zamfara

    02/07/2025 Duration: 03min

    A Najeriya mayaƙan sa kai a jihar Zamfara sun yi nasarar hallaka wasu daga cikin manyan kwamandojin ƴan bindigar da suka hana zaman lafiya a jihar, cikinsu har da Kachalla Ɗanbokolo da wasu tarin magoya bayansu. Domin sanin tasirin wannan nasara ga jama'ar yankin, Bashir Ibrahim Idris ya tattauba da masanin harkar tsrao, Dr Yahuza Getso.   Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar

  • Muhammad Adamu Dansitta kan shirin gwamnatin Najeriya na dasa bishiyoyi biliyan 20

    01/07/2025 Duration: 03min

    Gwamnatin Najeriya ta sha alwashin dasa itatuwa biliyan 20, a kokarin da take yi na magance gurgusowar hamada da tsananin zafi , har ma da sauyin yanayi. Mataimakin shugaban kasar Kashin Shetimma ne ya bayyana hakan, yayin da yake jawabi a wajen wani taroa  kasar Habasha. Game da tasirin wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Muhammad Adamu Dansitta. Dannan alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.

  • Issof Emoud kan sabuwar Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Nijar da kafa

    30/06/2025 Duration: 03min

    Majalisar Tuntuɓa da gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta kafa ta conseil consultatif na fara aiki a ranar Asabar 28 ga watan Yunin wannan shekara ta 2025, Majalisar mai kunshe da mambobi 194 an ɗaura mata nauyin bayar da shawarwari kan harokin da su ka shafi cigaban ƙasa da  kuma gayyato majalisa zartaswa domin amsa tambayoyi idan hakan ta kama. A kan haka Oumar Sani ya  tattauna da Hon. Issouf Emoud ɗan majalisa mai wakilta jihar Agadas.

  • Amb Abubakar Chika: cika shekaru 80 da sanya hannu kan yarjejeniyar samar da MDD

    26/06/2025 Duration: 03min

    Yau ake cika shekaru 80 da rattaɓa hannu kan yarjejeniyar da ta samar da Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a Birnin San Francisco da ke Amurka, a ranar 26 ga watan Yunin shekarar 1945. Bikin cika shekaru 80 din na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar mai wakilai 193 ke fuskantar kalubale da dama, waɗanda suka hada da makomar ta ko kuma ci gaban tasirinta baki ɗaya. Kan wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Abubakar Chika, tsohon jakadan Najeriya a Iran. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawarsu ta gudana..........

page 2 from 2